Kasashen Afirka Sun Jaddada Wajabcin Karfafa Aikin Gona
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i10747-kasashen_afirka_sun_jaddada_wajabcin_karfafa_aikin_gona
Shugabannin Kasashen Afirka Sun Jaddada Muhammcin Farfado Da Aikin Gona.
(last modified 2018-08-22T06:58:53+00:00 )
Sep 08, 2016 02:06 UTC
  • Kasashen Afirka Sun Jaddada Wajabcin Karfafa Aikin Gona

Shugabannin Kasashen Afirka Sun Jaddada Muhammcin Farfado Da Aikin Gona.

Kamfanin Dillancin Labarun Xinhua na Kasar Sin, ya nakalto a jiya alhamis cewa; A yayin taron shugabannin Afirka karo na biyu da aka yi a babban birnin kasar Kenya, Nairobi, sun jaddada wajabcin farfado da aikin gona domin samun abinci.

Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyata, da ya gabatar da jawabi a wurin bude taron ya ce; Farfado da aikin gona, wajibi ne domin bunkasa da ci gaban tattalin arziki a rayuwar zamantakewa a cikin nahiyar Afirka.

Shugaban na kasar ta Kenya ya bayyana cewa; Bunkasa Aikin gona zai tabbatar da tsaro ta fuskar abinci a nahiyar sannan kuma zai samar da aikin yi a tsakanin samari maza da mata.

Shugaban kasar Rwanda, Paul Kigame wanda shi ma ya gabatar da jawabin ya ce; Zuba hannun jari da za a yi a cikin harkokin noma za su daukaka da bunkasa rayuwar mutanen Afirka.