Kotun Kasar Kenya: Dalibai Mata Na Iya Sanya Hijabi A Kasar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i10828-kotun_kasar_kenya_dalibai_mata_na_iya_sanya_hijabi_a_kasar
Rahotanni daga kasar Kenya sun bayyana cewar wata kotun daukaka kara a kasar ta bayyana cewar dalibai mata musulmi a kasar suna iya sanya hijabi a lokacin da za su tafi makarantun na su a matsayin tufafin makarantar.
(last modified 2018-08-22T06:58:54+00:00 )
Sep 09, 2016 13:56 UTC
  • Kotun Kasar Kenya: Dalibai Mata Na Iya Sanya Hijabi A Kasar

Rahotanni daga kasar Kenya sun bayyana cewar wata kotun daukaka kara a kasar ta bayyana cewar dalibai mata musulmi a kasar suna iya sanya hijabi a lokacin da za su tafi makarantun na su a matsayin tufafin makarantar.

Jaridar  Daily Motion ta kasar Kenya ta bayyana cewar a cikin hukuncin da kotun ta fitar ta ce musulmin suna da damar sanya hijabi  su tafi makarantun su, kamar yadda kuma ta bukaci hukumar kula da ilmi ta kasar da ta tsara wasu sabbin dokoki dangane da tufafin 'yan makarantar wadanda ba za su nuna wariya ko cutarwa ga wani dalibi saboda addininsa ba.

Hukuncin kotun daukaka karar dai ya biyo bayan wani hukunci ne da wata kotu a kasar ta yanke a kwanakin baya inda ta haramta wa 'yan makaranta mata musulmi sanya hijabi din yayin da suke makarantar, lamarin da kotun daukaka karar ta ce babu laifi cikin hakan.

Batun haramcin sanyan hijabi a makarantar dai ya biyo bayan karar da wata makaranta ta kiristoci a kasar ta shigar ne inda ta bukaci da a hana 'yan mata  musulmi sanya hijabi din don a cewarsu sanya kaya daban-daban tsakanin daliban zai haifar da rashin jituwa da kyamar juna tsakanin daliban.