Girgizar Kasa A Kasar Tanzania Ta ci Rayukan Mutane 11
A kalla mutane 11 ne su ka kwanta dama sanadiyyar girgizar kasar da ta afku a gunudmar Bokoba da ke arewa maso yammcin kasar Tanzania.
A kalla mutane 11 ne su ka kwanta dama sanadiyyar girgizar kasar da ta afku a gunudmar Bokoba da ke arewa maso yammcin kasar Tanzania.
Babban jami'in 'yansanda a yankin da girgizar kasar ta faru, Augustine Aulomy ya ce; Mun kirga gawawwaki 11 da kuma wadanda su ka jikkata fiye da 100, da aka dauka zuwa asibiti.
Girgizar kasar mai karfi daraja 5,7 a ma'aunin Richard, ta afku ne a kasar ta Tanzania da kuma kasashen da su ke makwabtaka da ita a yau asabar. A kasashen Rwanda da Brundi da Uganda da Kenya an ji girgizar kasar kamar yadda cibiyar da ke kula da girgizar kasa ta Amurka ta bayyana.
Gidaje da gine-gine masu yawa sun zube kasa a garin Bokoba.