Maroko Tana Nan Akan Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Yaki Da Polisario
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i10861-maroko_tana_nan_akan_yarjejeniyar_tsagaita_wutar_yaki_da_polisario
Moroko Tana Aikin da Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Yaki
(last modified 2018-08-22T06:58:54+00:00 )
Sep 10, 2016 14:30 UTC
  • Maroko Tana Nan Akan Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Yaki Da Polisario

Moroko Tana Aikin da Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Yaki

Kamfanin Dillancin Labarun Faransa ya amabto jakadan Kasar Moroko a Majalalisar Dinkin Duniya, Umar Hilal yana cewa; Kasarsa tana nan akan riko da yarjejeniyar tsagaita wutar yaki da kungiyar Polisario ta yammacin sahara.

Umar Hilal ya ci gaba da cewa; Kasarsa tana cikin shirin ko ta kwana, sai dai tana kai zuciya nesa, sannan kuma tana riko da yarjejeniyar tsagaita wuta.

Jawabin na Jakadan Moroko a majalisar dinkin duniyar dai ya zo ne adaidai lokacin da ake nuna damuwa akan yiyuwar barkewar rikici tsakanin sojojin kasar da na mayakan kungiyar yammacin sahara ta Polisario.

Tun a 1991 ne aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta bisa shiga tsakanin majalisar dinkin duniya, tsakanin Moroko da mayakan kungiyar ta Polisario. Yarjejeniyar dai ta kawo karshen yakin shekaru 16 a tsakanin bangarorin biyu.