An Kashe 'yan ta'addar al-shabab biyu a kasar Somaliya
Sep 26, 2016 15:46 UTC
Dakarun Afirka Sun kashe 'yan al-shabab biyu
Dakarun tabbatar da tsaro na kasashen Afirka da ake kira ( Amsiom) sun kashe 'yan kungiyar al-shabab biyu a garin Kimaeo da ke kudancin kasar Somaliya.
Kamfanin dillancin Labarun Xinhua na kasar Sin ya nakalto cewa; kashe 'yan al-shabab din biyu ya biyo bayan gumurzun da aka yi ne a jiya lahadi wanda ya ci rayukan mutane 10.
Majiyar dakarun ta ( Amsiom) ta ce sun kashe 'yan kungiyar ta al-shabab biyu ne a lokacin da su ke share garin kimaeo da ke gabar ruwa daga 'yan ta'adda.
Rashin tsaro da ake fama a kasar ta Somaliya ya sa an dage zaben 'yan majalisa da aka shirya yi a ranar asabar din da ta gabata.
Tags