Muhimmancin Tattaunawa Tsakanin Gwamnatin Suda Da 'Yan hammayya A cikin Gida.
Sep 28, 2016 03:48 UTC
Shugaban Kasar Sudan, ya jaddada muhimmancin Tattaunawa Da 'Yan hamayya A cikin Gida.
Kamfanin Dillancin Labarun Xiunhua na kasar Sin, ya ambato shugaba Umar Hassan al-Bashir na Sudan yana yin kira ga 'yan hamayya a jiya talata, da a ci gaba da tattaunawar sulhu a cikin gida, ba a waje ba.
Shugaban na kasar Sudan ya kuma ce gwamnati tana son ganin an cimma matsaya ne wacce za ta kare manufofin dukkanin bangarorin biyu.
A ranar 10 ga watan Oktoba ne za a bude wani zango na tattaunawa a tsakanin gwamnati da kuma 'yan hamayyar kasar a birnin Khartum.
Tattaunawar dai ana yinta ne a tsakanin gwamnatin Khartum da kuma 'yan hamayyar daga yankunan Darfur da Blue Nile da Kurdufan ta kudu.
Tags