Ana ci gaba da Kashe Mutane A Kasar Afirka Ta Tsakiya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i11677-ana_ci_gaba_da_kashe_mutane_a_kasar_afirka_ta_tsakiya
Majalisar Dinkin Dunkiya ta Sanar da mutuwar mutane da yawa a Afrika ta tsakiya
(last modified 2018-08-22T06:59:00+00:00 )
Sep 28, 2016 03:53 UTC
  • Ana ci gaba da Kashe Mutane A Kasar Afirka Ta Tsakiya

Majalisar Dinkin Dunkiya ta Sanar da mutuwar mutane da yawa a Afrika ta tsakiya

Kafar watsa labaru ta  "Africa Time" ta ambato kakakin dakarun tabbatar da zaman lafiya na majalisar dinkin duniya a Afirka ta tsakiya, Vladimir Monteiro, yana cewa; A tsakiyar watan Satumba an sami mutuwar mutane tsakanin 10 zuwa 20 a garin Kouango da ke tsakiyar kasar.

Vladimir Monteiro ya kara da cewa 'yan tawayen Seleka  ne masu tada hargitsi a kauyen na Kouango, kuma suna ci gaba da kashe fararen hula da kona gidane a cikin wasu kauyuka.

Kakakin dakarun tabbatar da zaman lafiyar na majalisar dinkin duniyar ya kara da cewa; Da akwai dakaru 12,000 da su ke aiki da gwamnatin kasar ta Afirka ta tsakiya, a fadin kasar.

A shekarar 2013 ne kasar ta Afirka ta tsakiya ta fada rikicin kabilanci da addini wanda ya ci rayuka da dama.