RDC : Za'a Taimakawa Iyalen Wadandan Suka Mutu A Zanga-Zanga
Sep 29, 2016 08:36 UTC
Gwamnatin RD. Congo ta ce zata taimakawa iyalen wadanda suka mutu a zanga-zanga baya-bayan nan da $ Amurka 5,000 ko wannensu.
A cewar gwamnatin Kishasa za'a baiwa iyalen duk wani da ya rasa ransa a zanga-zanga da aka fuskanta a kasar a ranarkun 19 zuwa 20 ga watan nan na Satumba.
Ma'aikatar kiwan lafiya ta kasar ce keda nauyin rejistan iyalen tare da kwararen hujjoji, kasancewa tuni aka fara samun rahotanni toge a cikin lamarin.
Saidai babbar jam'iyyar adawa ta kasar ta ce taji takaicin rashin saka magoya bayan ta a cikin wannan tsarin.
Kimanin mutane 49 ne suka rasa rayukansu a borin kin jinin gwamnatin Josef kabila.
Tags