Adadin Wadanda Aka Kashe A Habasha Sun Karu
Oct 08, 2016 03:26 UTC
Karuwar Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati A Kasar Habasha
An kara samuwar wadanda su ka rasa rayukansu a kasar Habasha, bayan Zanga-zangar da aka yi a garin Bishopto da ke kudancin kasar.
Majiyar gwamnati ta ce adadin wadanda su ka rasa rayukansu a rikicin da kasar ta ke fuskanta sun kai 55, sai dai majiyar 'yan hamayya ta ce adadin sun dara haka da dama.
Masu zanga-zangar dai suna nuna kin amincewarsu ne da rashin adalcin da su ke fuskanta daga gwamnatin kasar a tsawon shekara da shekaru.
A cikin watannin bayan nan dai zanga-zanga kin jinin gwamnati ta tsananta a cikin kasar ta Habasha.
Tags