Somaliya: Asarar Rai Asanadin Tarwatsewar Mota Mai Makare Da Bom
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i12268-somaliya_asarar_rai_asanadin_tarwatsewar_mota_mai_makare_da_bom
Mutum Guda Ya Mutu A Somaliya Saboda harin ta'addanci
(last modified 2018-08-22T06:59:04+00:00 )
Oct 10, 2016 15:31 UTC
  • Somaliya: Asarar Rai Asanadin Tarwatsewar Mota Mai Makare Da Bom

Mutum Guda Ya Mutu A Somaliya Saboda harin ta'addanci

Jami'ian Tsaron Kasar Somaliya Sun sanar da fashewar wata mota mai makare da bama-bamai a birnin Mogadishu wanda ya yi sanadin mutuwar mutum guda.

Bugu da kari, wasu mutane 3 sun jikkata sanadiyyar tashin bom din.

Kamfanin Dillancin Labarun Xinhua ya ambato jami'an tsaron kasar suna cewa; tuni sun kame wani mutum guda wanda su ke zargi da hannu a shirya kai harin.

Kawo ya zuwa yanzu dai  babu wanda ya dauki nauyin kai harin, sai dai jami'an tsaron kasar na zargin kungiyar al-shabab.