Habasha: Ci gaba da yin Zanga-zangar Kin Jinin Gwamanti
Oct 19, 2016 08:45 UTC
Ana ci gaba da yin zanga-zanga A Habasha
Ana ci gaba da yin Zanga-zangar kin jinin gwamnati a kasar Habasha.
A yau laraba an yi zanga-zanga mai tsanani a yankin Oromo, sai dai gwamnatin kasar ta yi kira da a kawo karshenta.
Wasu rahotanni daga kasar sun ce jami'an tsaro sun kame wasu masu zanga-zanga da dama.
Ma'aikatar tsaron kasar ta Habasha ta ce, tana sa ido da bin diddigin hanyoyin sadarwar da masu zanga-zangar su ke amfani da ita.
Al'ummar Oromo dai suna yin Zanga-zanga ne domin nuna kin amincewarsu da abinda su ka kira rashin samar da daidaito ta fuskar tattalin arziki da raba mukamai a tsakanin 'yan kasa.
Mutane 55 ne aka kashe a zanga-zangar da aka yi a baya.
Tags