Kungiyar Tarayyar Afirka ta dauki kudirin kawo karshen kungiyar Ashabab a Somaliya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i13522-kungiyar_tarayyar_afirka_ta_dauki_kudirin_kawo_karshen_kungiyar_ashabab_a_somaliya
Ofishin Dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar Tarayyar Afirka (Amison) dake kasar Somaliya ya tabbatar da cewa za ta karya lagon kungiyar Ashabab a kasar baki daya.
(last modified 2018-08-22T06:59:12+00:00 )
Nov 07, 2016 07:35 UTC
  • Kungiyar Tarayyar Afirka ta dauki kudirin kawo karshen kungiyar Ashabab a Somaliya

Ofishin Dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar Tarayyar Afirka (Amison) dake kasar Somaliya ya tabbatar da cewa za ta karya lagon kungiyar Ashabab a kasar baki daya.

Ofishin ya ce Dakarun su dake jibke a yankuna daban daban na cikin kasar a shirye suke su karya lago da kuma tunkarar duk wata barazana na kungiyar Ashabab din kuma hakan ma ya zamanto wajibi domin tabbatar da tsaro a kasar.

Wannan sanarwa na zuwa ne yayin da aka nada Nuru Usman Suba garke a matsayin sabon Kwamandan kungiyar wanzar da zaman lafiya na tarayar Afirka a kasar Somaliyan da ake kira da Amisson.

Duk da cewa Kungiyar Amison din ta samu nasara da dama wajen tabbatar da tsaro a kasar Somaliyan, to amma har har yanzu kungiyar ta Ashabab na ci gaba da kai hare haren ta'addanci a kasar .