Togo: Taron Wasu Kasashen Afirka Akan Harkokin Tsaro
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i13810-togo_taron_wasu_kasashen_afirka_akan_harkokin_tsaro
Kasashe Biyar Na Yammacin Afirka Suna yin taro A Togo.
(last modified 2018-08-22T06:59:14+00:00 )
Nov 13, 2016 08:34 UTC
  • Togo:  Taron Wasu Kasashen Afirka Akan Harkokin Tsaro

Kasashe Biyar Na Yammacin Afirka Suna yin taro A Togo.

Kamfanin Dillacin Labarun Xinhua, ya ambato cewa; Jami'an tsaron, kasar Benin da Nijar da Burkina Faso, da Ivory Coast da Togo suna yin taro domin tattauna harkokin tsaro.

Jami'an tsaron kasashen biyar suna yin taron ne a birnin Lome inda su ke tattauna matsalar tsaro a cikin kasashen yammacin Afirka da kuma cikin kasashensu.

Jami'an tsaron kasashen suna kuma tattauna batun ta'addanci da fasakwaurin mutane da aikata manyan laifuka a cikn yankin na yammacin Afirka.

Wakilin kasar Togo a wurin taron Yark Damehane, ya bayyana cewa; Mahalarta taron sun daura azamar yin aiki tare a tsakaninsu domin fuskantar halin da ake ciki a yammacin Afirka.