Sudan : An Kara Wa'adin Tsagaita Wuta
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i16069-sudan_an_kara_wa'adin_tsagaita_wuta
Shugaban kasar Sudan Omar Hassan Al Bashir, ya sanar da tsawaita yarjejeniyar tsagaita bude wuta na tsawon wata guda a fadan da dakarunsa ke yi da ‘yan tawaye a yankin Darfur.
(last modified 2018-08-22T06:59:29+00:00 )
Jan 03, 2017 14:40 UTC
  • Sudan : An Kara Wa'adin Tsagaita Wuta

Shugaban kasar Sudan Omar Hassan Al Bashir, ya sanar da tsawaita yarjejeniyar tsagaita bude wuta na tsawon wata guda a fadan da dakarunsa ke yi da ‘yan tawaye a yankin Darfur.

Tun a watan Oktoban 2016 ne, bangarorin biyu suka amince da tsagaita bude wuta a yankunan kudancin Blue Nile da Kordufan, amma har yanzu ana samun rikici a Dafur.

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun bude wuta a Nertiti, yankin Darfur, in da suka kashe mutane 8 yawancinsu mata da aka bindige a cikin gida.

Tun a 2011 ne sabon fada ya barke tsakanin dakarun Sudan da ‘yan tawaye a Kordufan da Blue Nile, a lokacin da Sudan ta kudu ta balle daga kasar.

An dai dade ana kokarin sulhu domin samun zaman lafiya kuma wannan ne ya sa shugaban ya kara tsawaita tsagaita wuta a sakon sabuwar shekara domin bude kofar sasantawa da ‘yan tawayen a Darfur.