Kananan Yara Kimanin 60,000 Suna Fuskantar Barazanar Mutuwa A Somaliya
Jami'in Majalisar Dinkin Duniya mai kula da harkokin jin kai a yankin arewa maso gabashin nahiyar Afrika ya bayyana cewa: Kananan yara kimanin 60,000 ne suke fuskantar barazanar mutuwa a kasar Somaliya saboda rashin kayayyakin jin kan bil-Adama.
Jami'in Majalisar Dinkin Duniya mai kula da harkokin jin kai a yankin arewa maso gabashin nahiyar Afrika Peter de Clark matsalolin tashe-tashen hankula da fari da kuma ambaliyar ruwa da ake samu a yankuna daban daban na kasar Somaliya, hakan ya wurga mutane cikin halin kaka-ni ka yi, inda akwai mutane da yawansu ya doshi miliyan biyar da suke bukatar kayayyakin jin kai.
De Clark ya kara da cewa; Daga cikin mutanen da suke tsananin bukatar tallafin gaggawa a Somaliya akwai kananan yara kimanin 60,000 wanda sakacin aikewa da taimakon gaggawa cikin hanzari zai kai ga hasarar rayukansu.