Gwamnatin Nigeria Ta Amince Da Wani Sabon Tsarin Kiwon Lafiya A Kasar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i17706-gwamnatin_nigeria_ta_amince_da_wani_sabon_tsarin_kiwon_lafiya_a_kasar
Gwamnatin tarayyar Nigeria ta amince da wani sabon tsarin kiwan lafiya a kasar.
(last modified 2018-08-22T06:59:41+00:00 )
Feb 16, 2017 08:18 UTC
  • Gwamnatin Nigeria Ta Amince Da Wani Sabon Tsarin Kiwon Lafiya A Kasar

Gwamnatin tarayyar Nigeria ta amince da wani sabon tsarin kiwan lafiya a kasar.

Jaridar Premiumtimes ta nakalto ministan lafiya Isaac Adewole,  yana fadar haka a jiya Laraba bayan kammala taron majalisar ministoci na mako mako a fadar shugaban kasa. 

Isaac Adewole,  ya kara da cewa sabon tsarin kiwon lafiya a kasar, shi ne na ukku a tarihin kasar bayan tsari na 1988 da kuma ta 2004. Kuma wannan tsarin zai bada fifiko wajen tabbatar da cibiyoyin kiwon lafiya a kasar da kuma asbitoci suna aiki yanda yakamata. Sannan sabon tsarin zai maida kiwon lafiya a mataki na farko ya zama shine gintsikin kiwon lafiya a kasar.

Banda haka miunistan ya kammala da cewa sabon tsarin zai hada da tallafawa dukkan bangaririn kiwon lafiya da zasu kawo ci gaba a lafiyan mutanen kasar kai tsaye.