Guinea : An Sake Bude Makarantu Bayan Yajin Aikin Makwanni 3
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i17946-guinea_an_sake_bude_makarantu_bayan_yajin_aikin_makwanni_3
Rahotanni daga Guinea na cewa an sake bude makarantun boko a Guinea bayan kasancewarsu a rufe na tsawan makwanni uku saboda yajin aiki na malumen makarantu.
(last modified 2019-04-27T09:55:10+00:00 )
Feb 23, 2017 02:13 UTC
  • Guinea : An Sake Bude Makarantu Bayan Yajin Aikin Makwanni 3

Rahotanni daga Guinea na cewa an sake bude makarantun boko a Guinea bayan kasancewarsu a rufe na tsawan makwanni uku saboda yajin aiki na malumen makarantu.

Hakan dai ya biyo bayan yarjejeniyar da kungiyoyin malumane makarantun suka cimma da gwamnatin kasar a ranar Litini data gabata.

A ranar 1 ga watan Fabaruru na wannan shekara ne gwamnatin kasar ta dau matakin rufe makarantun saboda yajin aikin malumen da kuma zanga-zanga data ki karewa.

Yajin aiki dai ya hada kungiyoyin malumen makarantun dake neman karin albashi da kuma masu neman ayi masu daukar aiki ta din-dindin.

Alkalumen da mahukutan kasar suka fitar sun nuna cewa mutane biyar ne suka mutu kana wasu da dama ciki har da jami'an tsaro suka raunana a mumunar zanga zangar baya bayan nan a Conakry babban birnin kasar.