An karfafa matakan tsaro a jihar Kaduna
Bayan barkewar rikcin kabikanci a wani yanki na Jihar Kaduna, Gwamnati ta sanya dokar ta bace na tsahon sa'o'i 24
Cikin wata sanarwa da ya fitar a daren jiya Alkhamis,Kakakin Gwamnan Jihar Kaduna Samuel Aruwan ya bayyana cewa sakamakon rikicin da ya barke a wasu yankunan Jihar, an samu asarar rayukan Mutane akalla 14 domin dawo da kwanciyar hankali Gwamnati ta dauki matakin sanya dokar ta bace na sa'o'i 24 a yankunan domin baiwa Jami'an tsaro damar gudanar da aiyukansu.
Rahotanni sun bayyana cewa rikicin ya faru ne tsakanin Makiyaya da Manona a kan wurin kiyo da ban ruwan busashe, lamarin da ya kara matsin lamba ga magabatan jihar.
Shugaban 'yan sandar jihar kaduna Aghole Abeh ya sanar a jiya Alkhamis cewa sun tura Jami'an 'yan sanda na musaman a yankunan da rikicin ya auku, domin gawo karshen rikcin da kuma hana shi yaduwa zuwa sauren yankunan Jihar.
Bisa rahoton da Ma'aikatar dake kula da tashe-tashen hankula a Jihar ta Kaduna ta fitar , daga farkon wannan shekara ta 2017 zuwa yanzu kimanin Mutane 200 ne suka rasa rayukansu sanadiyar barkewar rikici a kudancin jihar ta Kaduna.