Gwamnatin Somaliya Ta Sanar Da Cewa: Kasar Tana Fuskantar Mummunar Matsalar Fari
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i18118-gwamnatin_somaliya_ta_sanar_da_cewa_kasar_tana_fuskantar_mummunar_matsalar_fari
Sabon shugaban kasar Somaliya ya bayyana cewa: Kasarsa tana fuskantar mummunar matsalar fari, don haka ya jaddada yin kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su hanzarta kawo dauki.
(last modified 2018-08-22T06:59:45+00:00 )
Mar 01, 2017 03:25 UTC
  • Gwamnatin Somaliya Ta Sanar Da Cewa: Kasar Tana Fuskantar Mummunar Matsalar Fari

Sabon shugaban kasar Somaliya ya bayyana cewa: Kasarsa tana fuskantar mummunar matsalar fari, don haka ya jaddada yin kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su hanzarta kawo dauki.

A bayanin da ya fitar a jiya Talata: Shugaban kasar Somaliya Muhammad Abdullahi Muhammad Farmajo ya bayyana tsananin damuwarsa kan yadda matsalar fari tayi mummunar tasiri kan al'ummar Somaliya a shekarar da ta gabata; Sakamakon haka ya jaddada yin kira ga kungiyoyin kasa da kasa kan hanzarta daukan matakin kawo dauki domin 'yantar da al'ummar Somaliya daga mummunar barazanar fari da take tunkararsu a wannan shekara.

Hukumar kula da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya a ranar Litinin da ta gabata ma ta fitar da bayanin gargadi kan yadda masifar fari ke barazana ga al'ummar Somaliya sakamakon rashin kyau amfanin gona a daminar data gabata lamarin da zai wurga rayuwar mutane kimanin miliyan 1.5 cikin mawuyacin halin rayuwa.