Somaliya: Yunwa Ta Kashe Mutane 110 A Cikin Sa'oi 48
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i18272-somaliya_yunwa_ta_kashe_mutane_110_a_cikin_sa'oi_48
Kamfanin Dillancin Labarun ( AFP) ya nakalto Pira ministan Somaliya na sanar da mutuwar mutane 110 saboda yunwa.
(last modified 2018-08-22T06:59:46+00:00 )
Mar 06, 2017 08:25 UTC
  • Somaliya: Yunwa Ta Kashe Mutane 110 A Cikin Sa'oi 48

Kamfanin Dillancin Labarun ( AFP) ya nakalto Pira ministan Somaliya na sanar da mutuwar mutane 110 saboda yunwa.

Pira ministan kasar ta Somaliya Khairi da ya fitar da bayani a ranar asabar ya fadi cewa; Mutanen da su ka mutu sun rika yin gudawa mai tsanani, a yankin kudancin kasar.

Pira ministan ya ci gaba da cewa; Wajibi ne ga mutane kasar ta Somaliya a duk inda su ke da su taimakawa 'yan'uwansu 'yan kasar mabukata da su ke fama da yunwa.

 Har  ila yau, pira ministan ya ci gaba da cewa; Aikin da ke gaban hukuma shi ne taimakawa mutanen da fama da yunwar, saboda farin da kasar ta ke fama da shi.

A yankin al-Bay na kasar mahukunta sun sanar da mutuwar mutane 69 mafi yawancinsu kananan yara da tsofaffi.

Tun a karshen watan Febrairu ne dai gwamnatin kasar ta Somaliya ta sanar da halin ko ta kwana saboda fari mai hatsari da kasar ta ke fama da shi.

Mutane miliya 3 ne dai farin ya jefa cikin yunwa kamar yadda kungiyoyin fararen hula su ka ambata.