Sudan: An Bukaci Neman Gudanar Da Bincike Akan Harin Makamai Masu Guba.
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i18300-sudan_an_bukaci_neman_gudanar_da_bincike_akan_harin_makamai_masu_guba.
Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira da a gudanar da bincike akan harin makamai masu guba a yankin Darfur.
(last modified 2018-08-22T06:59:47+00:00 )
Mar 07, 2017 09:18 UTC
  • Sudan: An Bukaci Neman Gudanar Da Bincike Akan Harin Makamai Masu Guba.

Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira da a gudanar da bincike akan harin makamai masu guba a yankin Darfur.

Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira da a gudanar da bincike akan harin makamai masu guba a yankin Darfur.

Wani jami'in majalisar dinkin duniya, Micheal Margary ya  yi ishara da harin na dabbanci da aka kai a yankin na Darfur, tare da cewa;" Rashin ghudanar da binciken bin kunya ne ga majalisar dinkin duniya."

A cikin watan Satumba da ya wuce ne majalisar dinkin duniyar ta gudanar da bincike da ya tabbatar da cewa sojojin gwamnati sun yi amfani da makamai masu guba a harin da su ka kai a Jabalu Murrah a yankin na Darfur.

Binciken ya kuma tabbatar da cewa mutane 200-250 ne su ka rasa raukansu sanadiyyar harin.