Azhar: Wajibi ne A Kare Hadin Kan Da Ke Tsakanin Kasashen Afirka.
Mar 08, 2017 08:58 UTC
Shugaban Azhar Ahmad Tayyib ya ce; Wajibi ne a tabbatar da kare hadin kan da ya ke a tsakanin kasashen nahiyar Afirka.
Sheikh Ahamd Tayyib wanda ya ke ganawa da manema labaru daga kasashen Afirka ya jaddada cewa; Kasashen Afirka suna da arziki da wadata da kuma dama mai yawa, don haka wajibi ne a yi amfani da su domin kyautata rayuwar al'umma.
Sheikh Ahmad Tayyib ya ci gaba da cewa; Samar da daidaito da yin adalci da girmama hakkokin mutane, su ne abin nema a cikin kasashen na Afirka.
Har ila yau, sheun na Azhar ya ce; Shiga hakkin wani, ya sabawa shari'a, sannan ya kara da cewa: Dukkanin addinai da kuma kyawawan al'adu na al'ummu, suna yi kira da a kawo karshen ayyukan ta'addanci a duniya.
Tags