Azhar: Wajibi ne A Kare Hadin Kan Da Ke Tsakanin Kasashen Afirka.
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i18336-azhar_wajibi_ne_a_kare_hadin_kan_da_ke_tsakanin_kasashen_afirka.
Shugaban Azhar Ahmad Tayyib ya ce; Wajibi ne a tabbatar da kare hadin kan da ya ke a tsakanin kasashen nahiyar Afirka.
(last modified 2018-08-22T06:59:47+00:00 )
Mar 08, 2017 08:58 UTC
  • Azhar: Wajibi ne A Kare Hadin Kan Da Ke Tsakanin Kasashen Afirka.

Shugaban Azhar Ahmad Tayyib ya ce; Wajibi ne a tabbatar da kare hadin kan da ya ke a tsakanin kasashen nahiyar Afirka.

Sheikh Ahamd Tayyib wanda ya ke ganawa da manema labaru daga kasashen Afirka ya jaddada cewa; Kasashen Afirka suna da arziki da wadata da kuma dama mai yawa, don haka wajibi ne a yi amfani da su domin kyautata rayuwar al'umma.

Sheikh Ahmad Tayyib ya ci gaba da cewa; Samar da daidaito da yin adalci da girmama hakkokin mutane, su ne abin nema a cikin kasashen na Afirka.

Har ila yau, sheun na Azhar ya ce; Shiga hakkin wani, ya sabawa shari'a, sannan ya kara da cewa: Dukkanin addinai da kuma kyawawan al'adu na al'ummu, suna yi kira da a kawo karshen ayyukan ta'addanci a duniya.