Somalia ta bukaci a binciki kisan 'yan gudun hijiranta a Teku
kasar Somalia ta bukaci Saudiya da ta gudanar da bincike kan kisan ‘yan gudun hijiran kasar da aka aikata a kan teku.
Ya zuwa yanzu dai babu wani cikakken bayani da aka fitar dangane maharan da suka kashe ‘yan gudun hijira sama da 40 a cikin jirgin ruwa da ke gabar tekun Yemen, Sai dai ana zargin ‘kawancan saudiya dake kaddamar da hare-haren wuce gona da irin kan Al'ummar kasar ta Yemen da kai harin
A ranar Juma'ar da ta gabata aka bindige ‘yan gudun hijiran Somalia da suka hada da mata da kanana yara 42 a cikin wani jirgin ruwa da ke kokarin tsallakawa zuwa Turai ta gabar tekun Yemen dake kalkashin ikon Gwamnatin kasar
Hukumar ‘yan gudun hijira ta Duniya ta ce akwai mutane akalla 80 da aka ceto bayan harin, inda 24 daga cikinsu ke cikin matsanancin hali.