Mutane da dama sun rasu sanadiyar fari a Somaliya
Matsalar fari da kasar Somaliya ta fuskanta ya yi sanadiyar mutuwar Mutane 26 cikin kwana guda kacal a wani yanki na kasar
Hukumar Telbijin da Radio na kasar Iran ya habarta cewa matsalar fari da kasar Somaliya ta fuskanta a shekarar Bana na ci gaba da kashe Mutane a kasar inda ciki kwana guda kacal Mutane 26 suka rasa rayukansu a yankin Gobaland dake kalkashin ikon 'yan ta'addar kungiyar Ashabab a kudancin kasar.
Rahoton ya ce baga mutanan da suka rasa rayukansu,Duban Mutane sun yi hijra sanadiyar karamcin abinci a yankin, kuma a halin da ake ciki kimanin Mutane Milyan shida da dubu 200 ne ke bukatar taimakon gaggawa a kasar.
Ko baya ga kasar Somaliyan akwai kasashe da dama na yankin Afirka da suka fuskancin matsalar fari a shekarar ta Bana, lamarin da ya sanya Saktare Janar na MDD kira ga Shugabanin kasashen Afirka da su dauki mtakan gaggauta domin kalu balantar matsalar ta karamcin abinci.