Sudan Ta Kudu : Hukumomi Ne Umul-Aba'insin Yunwa
-
Sudan ta kudu na daga cikin kasashen duniya da yunwa ke barazanawa al\\\\\\\'umma
Masu sharhi kan lamuran yau da kulun sun dora alhakin bala'in yunwa dake shafar dariruwan al'umma a Sudan ta kudu kan mahukuntan kasar.
Ana ganin dai idan tallafin da ake badawa na ceto rayukan jama'a ya gaza, to fa ya kamata a duba hanyoyin samar da zamen lafiya mai daurewa domin kawo karshen ukubar da jama'ar wannan kasa ke ciki a cewar Alan Boswell wani mai sharhi kan al'amuran Sudan ta kudun.
Ya kara da cewa ba banza ne ba yankunan dake fama da yunwa a Sudan ta Kudun suka kasance a wani rahoto da MDD ta fitar inda kabilar Nuer na jagoran 'yan tawaye Riek Machar da kuma kabilar Dinka inda dakarun gwamnatin Salva Kiir keda iko.
Dama kafin hakadiyar Amurka a MDD, Michele Sison ta gargadi kwamitin tsaro na MDDn akan abubuwan dake kara dagula al'amuran magance yunwa a Sudan ta Kudu, musamen yadda bangarorin dake rikici a kasar ke kawo cikas wajen isar da kayan agaji ga mabukata.