Wasu 'Yan Bindiga Sun Bude Wuta Kan Fararen Hula A Kasar Sudan
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i19074-wasu_'yan_bindiga_sun_bude_wuta_kan_fararen_hula_a_kasar_sudan
Wasu gungun 'yan bindiga sun bude wuta kan mai uwa da wabi kan wata kasuwa da ke lardin Kordofan ta Arewa da ke kasar Sudan, inda suka kashe mutane tare da jikkata wani adadi na daban.
(last modified 2018-11-18T05:33:40+00:00 )
Apr 03, 2017 01:06 UTC
  • Wasu 'Yan Bindiga Sun Bude Wuta Kan Fararen Hula A Kasar Sudan

Wasu gungun 'yan bindiga sun bude wuta kan mai uwa da wabi kan wata kasuwa da ke lardin Kordofan ta Arewa da ke kasar Sudan, inda suka kashe mutane tare da jikkata wani adadi na daban.

Shafin watsa labaran Al-Yaumus Sabi'i na kasar Masar ya habarta cewa: Wasu gungun mahara da suke cikin wasu tawagar motoci sun bude wuta kan jama'a a wata kasuwa da ke lardin Kordofan ta Arewa na kasar Sudan a jiya Lahadi, inda suka kashe mutane akalla bakwai tare da jikkata wani adadi na daban, sannan suka ari na kare.

Tun a shekara ta 2011 ne wani sabon gumurzu ya kunno kai tsakanin sojojin gwamnatin Sudan da na 'yan tawayen kasar a yankunan da suke lardunan Kordofan ta Kudu da na Arewa gami da Blue Nile lamarin da ke ci gaba da lashe rayukan jama'a musamman fararen hula.