Shugaban Kenya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hatsaniya A Lokacin Zabe
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i19640-shugaban_kenya_ya_gargadi_masu_tayar_da_hatsaniya_a_lokacin_zabe
Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta ya yi gargadin shiga kafar wando daya da duk wanda ya nemi tayar da wata hatsaniya a lokacin gudanar da zabukan 'yan majalisa a kasar.
(last modified 2018-08-22T06:59:59+00:00 )
Apr 20, 2017 13:18 UTC
  • Shugaban Kenya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hatsaniya A Lokacin Zabe

Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta ya yi gargadin shiga kafar wando daya da duk wanda ya nemi tayar da wata hatsaniya a lokacin gudanar da zabukan 'yan majalisa a kasar.

Kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar da rahoton cewa, a lokacin da yake gabatar da wani jawabi a yau, shugaban kasar Kenya Uhuru enyatta ya bayyana cewa, ba zai iya jure wa tayar da duk wata tashin-tashina ba  alokacin zaben 'yan majalisa mai zuwa, a kan haka za a dauki dukkanin matakai na doka domin tabbatar da cewa an yi komai bisa ka'ida.

A ranar 8 ga watan Agustan wanann shekara ta 2017 ce za a gudanar da zaben 'yan majalisar dokoki a kasar Kenya.

Kimanin mitane miliyan 19 ne daga cikin al'ummar kasar Kenya miliyan 45 suka cancanci kada kuri'a.