Ziyarar Shugaban Kasar Masar A Saudiya
Shugaban Kasar Masar ya fara Ziyarar aiki na kwanaki biyu a kasar Saudiya
Tashar Telbijin din Almayadeen ta kasar Labnon ta habarta cewa a wannan Lahadi, Shugaban kasar Masar Abdulfatah Alsese ya amsar goron gayyatar Shugaban kasar Saudiya Salman bn Abdul-Aziz da nufin farfado da alaka dake tsakanin buranen Riyad da Alkahira.
A cewar Alaae Yusuf mai magana da yawun fadar Shugaban kasar Masar, za a gudanar da zama tsakanin shugabanin kasashen Masar da Saudiya a yayin wannan ziyara, kuma kafin hakan, magabatan Saudiya sun yi alkawarin saka hanun jari na tsabar kudi biliyan 25 na dalar Amurka.
A nasa bangare Ministan harakokin wajen kasar Masar Samih Shukri ya tabbatar da cewa a yayin zaman magabatan kasashen biyu za a tattauna kan yanayi da kuma rikici na kasashen Siriya, Yemen, da Libiya.
A Watanin baya-baya nan dai danganta tayi tsami tsakanin kasashen biyu, bayan da kasar Masar ta jefa kuri'ar kin amincewa da kudirin da kasar Saudiya ta gabatar a gaban kwamitin tsaron MDD dangane da kasar Siriya, lamarin da ya sanya magabatan na Saudiya suka dakatar da sayar wa Masar din Man fetir gami da tallafin da suke bata.