Najeriya : An Kai Jerin Hare-Hare Kunan Bakin Wake A Maiduguri
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i19830-najeriya_an_kai_jerin_hare_hare_kunan_bakin_wake_a_maiduguri
Rahotanni daga Najeriya na cewa wasu jerin hare haren kunar bakin wake uku sunyi sanadin mutuwar mutun guda da kuma raunana wasu gomman mutane a wajen Maiduguri.
(last modified 2018-08-22T07:00:01+00:00 )
Apr 26, 2017 06:43 UTC
  • Najeriya : An Kai Jerin Hare-Hare Kunan Bakin Wake A Maiduguri

Rahotanni daga Najeriya na cewa wasu jerin hare haren kunar bakin wake uku sunyi sanadin mutuwar mutun guda da kuma raunana wasu gomman mutane a wajen Maiduguri.

Majiyoyin tsaro dana agaji sun shaidawa masu aiko da rahotanni cewa mata uku ne suka kai hare-haren a safiyar Larabar nan.

Bayanai daga yankin na cewa 'yan kunnar bakin waken sun tarwatse ne kafin suka kai inda suka doshi kai harin.

Wannan harin dai na zuwa ne kwanaki biyu bayan wani harin bom da ya yi sanadin mutuwar wasu dakarun hadin gwiwa hudu a yankin.