Rikicin Kabilanci Ya Lashe Rayukan Mutane Masu Yawa A Kasar DR Congo
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i19850-rikicin_kabilanci_ya_lashe_rayukan_mutane_masu_yawa_a_kasar_dr_congo
Majiyar dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya da ke Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo ta bayyana cewa: Akalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu sakamakon bullar rikicin kabilanci a lardin Kasai da ke tsakiyar kasar ta Dimokaradiyyar Congo.
(last modified 2018-08-22T11:30:01+00:00 )
Apr 27, 2017 05:49 UTC
  • Rikicin Kabilanci Ya Lashe Rayukan Mutane Masu Yawa A Kasar DR Congo

Majiyar dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya da ke Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo ta bayyana cewa: Akalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu sakamakon bullar rikicin kabilanci a lardin Kasai da ke tsakiyar kasar ta Dimokaradiyyar Congo.

A bayanin da majiyar dakarun wanzar da zaman lafiya da sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ta fitar a jiya Laraba yana dauke da bayanin cewa: Rikicin kabilanci da ya kunno kai a yankin Mungamba da ke lardin Kasai a tsakiyar kasar Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo tun daga ranar 19 ga wannan wata na Aprilu zuwa yanzu, an samu hasarar rayukan mutane akalla 20 tare da na tarin dukiyoyi.

A gefe guda kuma majiyar rundunar 'yan sandan kasar ta Dimokaradiyyar Congo ta sanar da cewa: A halin yanzu jami'an 'yan sanda sun samu nasarar shawo kan rikicin tare da gudanar da sintiri a yankin da nufin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali.