Gwamnatin Sudan Ta Kudu Ta Kori Ma'aikatan Tashar Aljazeera Daga Kasar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i19994-gwamnatin_sudan_ta_kudu_ta_kori_ma'aikatan_tashar_aljazeera_daga_kasar
Hukumar da ke kula da kafofin yada labarai a kasar Sudan ta kudu, ta sanar da korar ma'aikatan tashar Aljazeera mallakin gwamnatin kasar Qatar, saboda yada rahotanni na karya a kan kasar.
(last modified 2019-08-10T14:54:46+00:00 )
May 02, 2017 06:45 UTC
  • Gwamnatin Sudan Ta Kudu Ta Kori Ma'aikatan Tashar Aljazeera Daga Kasar

Hukumar da ke kula da kafofin yada labarai a kasar Sudan ta kudu, ta sanar da korar ma'aikatan tashar Aljazeera mallakin gwamnatin kasar Qatar, saboda yada rahotanni na karya a kan kasar.

Kamfanin dillancin labaran Irna ya bayar da rahoton cewa, babban daraktan hukumar kula da kafofin yada ta kasar Sudan ta kudu Lija Alir Kwaye ya sanar a daren jiya cewa, sun dakatar da dukkan ayyukan ma'aikatan tashar Aljazeera na bangaren turanci a kasar, sakamakon gudanar da aiki da ya saba wa aikin jarida.

Alira ya ce, tashar Aljazeera ta bayar da rahotanni da suke kara azuzuta wutar rikici a cikin kasar domin cimma wasu manufofi na siyasa, wanda hakan ke yin sanadiyyar mutuwar mutane, wannda hakan a cewarsa ya sabawa kaida ta aikin jarida,a  kan haka gwamnatin Sudan ta kudu dauki matakin da ya dace a kan ma'aikatan wanann tasha a cikin kasarta.