An Cafke Mambobin Kungiyar (Daesh) ISIS A Morocco
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i20276-an_cafke_mambobin_kungiyar_(daesh)_isis_a_morocco
jami'an tsaron kasar Morocco sun samu nasarar damke wasu daga cikin mambobin kungiyar 'yan ta'adda ta Daesh a kasar.
(last modified 2018-08-22T11:30:05+00:00 )
May 11, 2017 11:58 UTC
  • An Cafke Mambobin Kungiyar (Daesh) ISIS A Morocco

jami'an tsaron kasar Morocco sun samu nasarar damke wasu daga cikin mambobin kungiyar 'yan ta'adda ta Daesh a kasar.

Kamfanin dillancin labaran Xin Huwa ya nakalto daga ma'aikatar harkokin cikin gida  ta kasar Morocco cewa, rundunar yaki da ta'addanci ta kasar ta cafke mutane 6 mambobin kungiyar Daesh, wadanda suke da kwarewa a wajen hada bama-bamai, da kuma tayar da su, bayan samun horo daga wasu 'yan ta'adda tafkfiriyya da ke yaki a kasashen Syria da Iraki.

Bayanin ya ce mutanen suna cikin shirin kaddamar wasu munanan hare-haren bama-bamai a wasu muhimamn wurare a cikin kasar ta Morocco.

A cikin shekara ta 2016, jami'an tsaron Morocco sun sanar da kame 'yan ta'addan wahabiyya takfiriyya 273 a kasar, da suke da alaka da kungiyar ISIS.