An Kafa Gwamnatin Hadin Kan Kasa A Kasar Sudan
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i20296-an_kafa_gwamnatin_hadin_kan_kasa_a_kasar_sudan
Gwamnatin Kasar Sudan ta bada sanarwan kafa sabuwar gwamnarin wacce ta kari gawamnatin hadin kan kasa
(last modified 2019-03-07T02:07:59+00:00 )
May 11, 2017 23:12 UTC
  • An Kafa Gwamnatin Hadin Kan Kasa A Kasar Sudan

Gwamnatin Kasar Sudan ta bada sanarwan kafa sabuwar gwamnarin wacce ta kari gawamnatin hadin kan kasa

Tashar television ts sky news ta bayyana cewa shugaban umar hassan al-bashir ya nada Hasbu Muhammad abdurrahman a matsayin mataimakin shugaban kasa, kuma a yau jumma'a ce ake saran sabuwar majalisar ministocin kasar zata yi rantsuwar kama aiki.  

Majiyar ta kara da cewa Mohammad Hassan almirgani shi ne aka nada a matsayin mataimakin shugaban kasa na farko, sai kuma Ibrahim Mahmood  Hamid, Musa Muhammad Ahmad , Abdurrahman Sadikul Mahdi  duk an nada su ne a  matsayin masu bawa shugaban kasa shawara.

Banda haka shugaba Albashir ya nada Bakri Hassan Saleh a kan kujerar Priminista, kuma kafin haka shi ne mataimakin shugaban kasa na farko.

Shugaban Umar ya bayyana cewa gwamnatin hadin kan kasa da kuma jami'anta da ya dana duk sun cancanci mukaman da aka basu, sai dai Priministan ya  bayyana cewa majalisar dokokin kasar har yamzu bata amince da ministoci guda 6 ba