D.R Kongo : Karamcin Abinci Na Barazana Ga Yara 400,000
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i20704-d.r_kongo_karamcin_abinci_na_barazana_ga_yara_400_000
Asusun kula da yara kankanan yara na MDD wato Unicef ya yi kururuwar cewa yara kimanin 400,000 ke fuskantar barazanar matsananciyar yinwa a yankin Kasai na Jamhuriya Demukuradiyyar Kongo.
(last modified 2019-04-27T09:55:10+00:00 )
May 25, 2017 06:46 UTC
  • D.R Kongo : Karamcin Abinci Na Barazana Ga Yara 400,000

Asusun kula da yara kankanan yara na MDD wato Unicef ya yi kururuwar cewa yara kimanin 400,000 ke fuskantar barazanar matsananciyar yinwa a yankin Kasai na Jamhuriya Demukuradiyyar Kongo.

Matsalar na kara kamari ne a cewar Asusun na Unicef saboda rikicin dake ci gaba da faruwa a yankin.  

A rahoton data fitar jiya Laraba Unicef ta nuna matukar damuwa akan yanayin da ake ciki a yankin a watannin baya bayan nan wanda ta ce tana bukatar kudade sama da Dala Milyan arba'ín cikin gaggawa domin tunkarar matsalar.

Tun kafin barkewar rikici a yankin dama Kasai na daya daga cikin yankunan dake fama da talauci a wannan kasa ta D.R Kongo.