An Zargi Gwamnatin Kenya Da Take Hakkokin 'Yan Jarida A Kasar
Kungiyoyin kare hakkin bil adama na kasa da kasa sun zargi gwamnatin kasar Kenya da take hakkokin 'yan jarida masu zaman kansu a kasar.
Jaridar Lomond ta kasar Faransa ta bayar da rahoton cewa, wakilan kungiyoyin kare hakkin bil adama da ke birnin Nairobi sun bayyana yanayin da 'yan jarida suke ciki a kasar Kenya da cewa yanayi mai hadari, sakamakon irin barazanar da ake yi wa rayukansu.
Rahoton ya ce gwamnatin kasar ta kara daukar tsauraran matakai a kan ayyukan da 'yan jarida masu zaman kansu suke gudanarwa a kasar ne a daidai lokacin da zabukan kasar ke karatowa.
Tun a ranar 28 ga watan mayu da ya gabata ne aka bude yakin neman zabe a fadin kasar, a ranar 8 ga watan Agusta mai zuwa ne za a gudanar da zaben shugaban kasa, da na 'yan majalisar dokoki da kuma na gwamnoni a kasar ta Kenya.