INEC Ta Yi Wa Sabbin Jam'iyyun Siyasa 5 Rajista A Nijeriya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i21128-inec_ta_yi_wa_sabbin_jam'iyyun_siyasa_5_rajista_a_nijeriya
Hukumar zabe mai zaman kanta a Nijeriya, INEC, ta sanar da yin rajista wa wasu sabbin jam'iyyun siyasa su biyar a kasar don fafatawa a zabubbukan da za a gudanar nan gaba a kasar musamman ma dai na shekara ta 2019 mai zuwa.
(last modified 2018-08-22T07:00:13+00:00 )
Jun 08, 2017 00:52 UTC
  • INEC Ta Yi Wa Sabbin Jam'iyyun Siyasa 5 Rajista A Nijeriya

Hukumar zabe mai zaman kanta a Nijeriya, INEC, ta sanar da yin rajista wa wasu sabbin jam'iyyun siyasa su biyar a kasar don fafatawa a zabubbukan da za a gudanar nan gaba a kasar musamman ma dai na shekara ta 2019 mai zuwa.

Kakakin hukumar  ta INEC, Adedeji Soyebi, ne ya sanar da  hakan a wata sanarwa da ya fitar inda ya ce hukumar ta amince ta yi rajista wa wasu jam'iyyun siyasa su biyar da suka gabatar da bukatarsu, wanda hakan ya sanya a halin yanzu akwai jam'iyyun siyasa 45 kenan a Nijeriyan.

Sanarwa ta kara da cewa sabbin jam'iyyun da aka yi musu rajistan dai su ne:

(1). Young Progressive Party (YPP).

(2). Advanced Peoples Democratic Alliance (APDA).

(3). New Generation Party of Nigeria (NGP).

(4). All Democratic Peoples Movement (ADPM).

(5). Action Democratic Party (ADP).

A shekaran jiya Talata ce shugaban hukumar zaben , Farfesa Mahmood Yakubu ya sanar da cewa bayan taron da manyan kwamishinonin hukumar za su gudanar a jiya Laraba a Kaduna za a sanar da sunayen sabbin jam'iyyun da aka yi musu rajistan bayan bukatar hakan da kimanin jam'iyyun siyasa 95 suka gabatar wa hukumar na suna so a yi musu rajistan.