Ruwanda : Kagame Zai Sake Tsayawa Takara
Jun 18, 2017 11:31 UTC
Jam'iyyar FPR mai mulki a Ruwanda ta sake tsaida shugaban kasar mai ci Paul Kagame, a matsayin dan takararta a zaben shugabancin kasar na watan Agusta mai zuwa.
Mista Kagame, mai rikeda ragamar shugabancin kasar tun bayan kisan kiyashin 1994, zai sake takara a karo na uku.
Hakan dai na nufin Kagame zai ci gaba da mulkin kasar har zuwa 2034 idan ya sake lashe babban zaben, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada a kwaskwarimar da akayi masa a shekara 2015.
Matakin Paul Kagame na sake tsayawa takara a zaben kasar dake tafe na shan suka daga Amurka, da kuma 'yan adawa na kasar.
Tags