Rasha Ta Meka Jiragen Yaki Ga Kasar Masar
Rasha ta sanar da mekawa kasar Masar wasu Jiragen Yaki Samfarin K-52
Kamfanin dillancin Labaran Rambler na kasar Rasha ya nakalto majiyar tsaron kasar na cewa bisa yerjejjeniyar sayan makamai tsakanin kasashen Rasha da Masar, kasar ta meka wasu jiragen yaki samfarin K-52 ga magabatan kasar ta Masar, rahoton ya ce wakilan Dakarun saman Masar ne suka karbi jiragen a cibiyar tsaro ta garin Arsenyev dake kusu maso gabashin kasar ta Rasha.
Har ila yau rahoton ya ce a halin yanzu akwai wani gungun Soja na mtukan jiragen yaki na Masar dake karbar horo na musaman a cibiyar tsaron garin na Arsenyev.
A shekarar 2015 ne Kamfanin kirar Jiragen yakin Rasha ya kula yarjejjeniyar sayarwa Masar jirgen yaki samfarin K-52 guda 46 kuma shirin meka jiragen zai kamala kafin karshen wannan shekara ta 2017 da muke ciki.