Tsohon Gwamnan Jihar Taraba A Nigeria Ya Mutu
Tsohon gwamnan jihar Taraba a arewa maso gabcin Nigeria Danbaba Sunrai ya rasu a wani asbiti a Amurka a jiya Laraba
Jaridar Daily trus ta Nigeria ta bayyana cewa tsohon gwamnan wanda ya yi hatsari da jirgin da yake tukawa dakansa a cikin watan Octoban shekara ta 2012 ya mutu a wani asbiti a birnin Houston na jihar Florida a kasar Amurka a jiya Laraba.
Mr Emmanuel Bello babban mai bawa gwamnan jihar Taraba Darius Ishaku shawara kan al-amuran hulda da jama'a ya tabbatar wannan labari wa kamfanin dillancin labarai na Nigeria NAN.
Sutai dan shekara 56 a duniya yana jinya tun bayan hatsarin na watan Octoba, a asbitoci daban daban a ciki da wajen kasar, kuma a halin yanzu ana shirye shiryen dawo da gawarsa zuwa gida nan kusa.