An Hallaka Mayakan Al-shabab Shida A Somaliya
Dakarun Tsaron Somaliya sun hallaka mayakan kungiyar Ashabab 6 a kudancin kasar
Kamfanin dillancin Labaran Xin Huwa na kasar China ya nakalto Abdullahi Ali Anwad Babban Dakarun tsaron kasar Somaliya na cewa Mayakan kungiyar Ashabab sun hai farmaki barikin Sojojin kasar na yankin Shabul wusta dake kudancin kasar , a yayin fafatwar Sojojin kasar sun samu nasarar hallaka mayakan Ashabab din guda shida tare da jikkata wasu da dama na daban daga cikinsu.
Anwad ya kara da cewa a bangaren Sojojin kasar Sun rasa Mutum guda, a farkon wannan maku ne Dakarun kasar suka bayyana shirisu na fara kai farmaki kan mayakan kungiyar Ashabab da nufin kakkabe su daga wannan yanki.
A 'yan kwanakin baya bayan nan mayakan Ashabab din sun tsananta kai hare-hare a kan Dakarun kasar ta Somaliya da kuma Dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar Tarayyar Afirka dake cikin kasar.