Najeriya: Daruruwan 'Yan boko haram Sun Mika Kawukansu.
Jul 04, 2017 02:16 UTC
A jiya litinin ne dai 'yan kungiyar ta boko haram 700 su ka mika kawukansu ga sojojin Najeriya a jahar Borno.
A jiya litinin ne dai 'yan kungiyar ta boko haram 700 su ka mika kawukansu ga sojojin Najeriya a jahar Borno.
Kamfanin dillancin labarun Xinhua na kasar Sin, ya amato babban hafsan hafsoshin kasar ta Najeriya, Tukur Buratai yana sanar da mika wuyan 'yan boko haram din.
Bugu da kari Buratai ya ci gaba da cewa baya da wannan adadin, da akwai wasu 'yan kungiyar ta boko haram da su ke mika kawukan nasu ga sojoji.
A halin da ake ciki a yanzu da kawai 'yan wannan kungiyar su 1400 da ake tsare da su a arewa maso gabacin kasar.
Tags