Somaliya Tayi Hasarar Milyoyin Daloli Sakamakon Yankewar Internet
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i22040-somaliya_tayi_hasarar_milyoyin_daloli_sakamakon_yankewar_internet
Yankewar sadarwar yanar Gizo yayi sanadiyar hasarar sama da miliyan dari na dalar Amurka ga tattalin arzikin kasar Somaliya
(last modified 2019-03-18T05:42:56+00:00 )
Jul 09, 2017 11:12 UTC
  • Somaliya Tayi Hasarar Milyoyin Daloli Sakamakon Yankewar Internet

Yankewar sadarwar yanar Gizo yayi sanadiyar hasarar sama da miliyan dari na dalar Amurka ga tattalin arzikin kasar Somaliya

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Gwamnatin kasar Somaliya ta bayyana cewa yawan yankewar sadarwar yanar gizo cikin makunni biyu a kasar yayi sanadiyar hasarar milyan goma na $ a ko wace rana.

Ministan sadarwar kasar Abdi Anshor Hasan ya ce daga lokacin da aka fara yanke sadarwar yanar gizo zuwa yanzu kasar ta yi hasarar milyon 130 a bangaren tattalin arzikin kasar, ko baya ga hakan, yankewar Internet din ya janyo fishin Al'ummar kasar kuma yayi tasiri sosai a tsakiya da kudancin kasar daga ciki har da Magadushu babban birnin kasar.

Kasar Somaliya dai na daga cikin kasashen 4 da MDD ta bayyana su a matsayin masu fama da karamcin abinci sakamakon fari da kuma yaki, kasashen ukun sun hada da Yemen, Sudan ta kudu da Najeriya.