Somaliya: An Rusa Wata Cibiyar al-Shabab A Kudancin Somaliya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i22470-somaliya_an_rusa_wata_cibiyar_al_shabab_a_kudancin_somaliya
Kamfanin dillancin labarun Xinhua na kasar Sin ya ce rundunar hadin gwiwa ta sojojin Somaliya da dakarun zaman lafiya na Afirka ne su ka kai harin a kusa da garin Tortoro a kudancin kasar.
(last modified 2018-08-22T07:00:26+00:00 )
Jul 22, 2017 07:39 UTC
  • Somaliya: An Rusa Wata Cibiyar al-Shabab A Kudancin Somaliya

Kamfanin dillancin labarun Xinhua na kasar Sin ya ce rundunar hadin gwiwa ta sojojin Somaliya da dakarun zaman lafiya na Afirka ne su ka kai harin a kusa da garin Tortoro a kudancin kasar.

Kamfanin dillancin labarun Xinhua na kasar Sin ya ce rundunar hadin gwiwa ta sojojin Somaliya da dakarun zaman lafiya na Afirka ne su ka kai harin a kusa da garin Tortoro a kudancin kasar.

A wani bayani da rundunar tabbatar da zaman lafiya ta Afirka a Somalia ta fitar ta ce; Shakka babu rusa sansanin zai rage karfin da 'yan ta'addar su ke da shi wajen kai hare-hare akan al'ummar Somaliya.

Kungiyar ta'addanci ta al-shabab tana a matsayin babbar barazana ga tsaron Somalia da kuma sauran kasashen makwabta.