Fadar Shugaban Najeriya Ta Wallafa Hoton Buhari
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i22524-fadar_shugaban_najeriya_ta_wallafa_hoton_buhari
Fadar shugaban kasa a Najeriya, ta wallafa a shafinta na Twitter hoton shugaban kasar Muhammadu Buhari dake jinya a birnin Landan.
(last modified 2019-04-27T09:55:10+00:00 )
Jul 24, 2017 01:11 UTC
  • Buhari da wasu gwamnoni da kuma wasu jiga-jigan APC a birnin Landan. Hoto : Fadar shugaban kasa Najeriya
    Buhari da wasu gwamnoni da kuma wasu jiga-jigan APC a birnin Landan. Hoto : Fadar shugaban kasa Najeriya

Fadar shugaban kasa a Najeriya, ta wallafa a shafinta na Twitter hoton shugaban kasar Muhammadu Buhari dake jinya a birnin Landan.

A watan Mayun daya gabata ne shugaba Buhari  ya sake komawa birnin Landan domin yin jinya, saidai tun lokacin ne yau sama da wata biyu ba'a sake ganinsa ba a bainar jama'a.

Har yanzu dai ba'a bayyana hakikanin cutar dake damun Buhari mai shekara 74 ba. 

A cewar fadar shugaban kasar, Buhari ya gana da wata tawa tawagar gwamnoni da wasu mukaraban jam'iyyarsa ta APC da yammacin jiya Lahadi.

Sanarwar da fadar shugaban ta wallafa a shaffinta na Twitter ta ce shugaban yana isar da kyakyawan fata ga dukkan 'yan kasar, kana kuma zai koma kasar da zarar likitocinsa sun bashi umurni.