Najeriya: Akalla Mutane 8 Ne Su ka Mutu A Harin Maiduguri
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i22540-najeriya_akalla_mutane_8_ne_su_ka_mutu_a_harin_maiduguri
Kamfanin dillancin labarun Associated Press ya ambato majiyar tsaron Najeriya na cewa harin da aka kai da bom a jiya a sansanin 'yan gudun hijira a Maiduguri ya ci rayukan mutane 8 da jikkata wasu 11
(last modified 2018-08-22T07:00:26+00:00 )
Jul 24, 2017 14:31 UTC
  • Najeriya: Akalla Mutane 8 Ne Su ka Mutu A Harin Maiduguri

Kamfanin dillancin labarun Associated Press ya ambato majiyar tsaron Najeriya na cewa harin da aka kai da bom a jiya a sansanin 'yan gudun hijira a Maiduguri ya ci rayukan mutane 8 da jikkata wasu 11

Kamfanin dillancin labarun Associated Press ya ambato majiyar tsaron Najeriya na cewa harin da aka kai da bom a jiya a sansanin 'yan gudun hijira a Maiduguri ya ci rayukan mutane 8 da jikkata wasu 11.

Birnin Maiduguri yana daga cikin wuraren da 'yan ta'adda su ka fi kai wa hare-haren, inda su ka fi amfani da mata wajen kai harin kunar bakin wake.

Shekaru 8 kenan a jere da kungiyar bokoharam ta kai hare-hare a cikin yankuna daban-daban na kasar, sai dai a cikin watannin bayan nan hare-haren sun takaita a jahar Borno.