Najeriya: An Sace Motar Safa Mai Dauke Da Mutane 16
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i23006-najeriya_an_sace_motar_safa_mai_dauke_da_mutane_16
Kamfanin dillancin labarun Faransa ya nakalto cewa; Masu dauke da makamai sun tsare motar ne a kusa da birnin Port Harcout inda su ka yi garkuwa da mutanen cikinta 16
(last modified 2018-08-22T07:00:30+00:00 )
Aug 08, 2017 07:41 UTC
  • Najeriya: An Sace Motar Safa Mai Dauke Da Mutane 16

Kamfanin dillancin labarun Faransa ya nakalto cewa; Masu dauke da makamai sun tsare motar ne a kusa da birnin Port Harcout inda su ka yi garkuwa da mutanen cikinta 16

Majiyar 'yan sanda a garin na Por Harcourt sun tabbatar da faruwar lamarin, sannan kuma su ka sanar da cewa sun fara binciken ganon maharan.

Kawo ya zuwa yanzu dai babu cikakken bayani akan ko su waye maharan.

Satar mutane domin karbar fansa ta zama ruwan dare a cikin wasu yankuna na Najeriya.

Watannin baya ne dai jami'an tsaron kasar su ka kama Evans wanda ya shahara da satar mutane domin karbar fansa.