Somaliya: An Kashe Wani Babban Kwamandan al-Shabab
Majiyar gwamnatin kasar ta Somaliya ta sanar da cewa; Wanda aka kashe din yana da hannu a hare-hare na ta'addanci a cikin babban birnin kasar Magadishu.
Bayanin da ma'aikatar sadarwa ta kasar Somaliyan ta fitar a jiya alhamis ya kunshi cewa; A cikin makwanni biyu da su ka gabata, jami'an tsaron kasar sun yi nasarar rusa daya daga cikin gungun 'yan ta'addar da kuma kashe kwamandansu da ake kira da al-jibal.
Shugaban kasar ta Somaliya Muhammad Abdullahi Muhammad, ya bai wa sojojin kasar umarni da su yi aiki tare da sojojin kasa da kasa wajen kai hari a yankin " Banadir" da ke birnin Magadishu.
Kungiyar ta al-shabab mai alaka da al-ka'ida tana ci gaba da zama barazana ga kasar ta Somaliya da kuma kasashen makwabta.