Ranar Haihuwar Mugabe Ta Zama Ranar Hutu A Zimbabwe
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i23364-ranar_haihuwar_mugabe_ta_zama_ranar_hutu_a_zimbabwe
Ranar 21 ga watan Fabrairu wacce ta yi daidai da ranar haihuwar shugaba Robert Mugabe, zata kasance hutu a ko wacce zagayowarta a wannan kasa.
(last modified 2018-08-22T11:30:34+00:00 )
Aug 20, 2017 11:15 UTC
  • Ranar Haihuwar Mugabe Ta Zama Ranar Hutu A Zimbabwe

Ranar 21 ga watan Fabrairu wacce ta yi daidai da ranar haihuwar shugaba Robert Mugabe, zata kasance hutu a ko wacce zagayowarta a wannan kasa.

Jaridar Herald mallakin gwamnatin kasar ta Zimbabwe ta rawaito labarin cewa za'a dinga hutu a ko wacce zagayowar ranar haihuwar shugaban kasar

Robart Mugabe dan shekaru 93 na shugabancin wannan kasar ta Zimbabwe ne tun cikin 1980.

Lamarin ya bayyana ware kebe wannan ranar a matsayin nuna karamci ne ga shugaban kasar kamar yadda jaridar ta rawaito ministan cikin gidan na kasar na fada.

Duk da yawan shekarunsa Mugabe ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takara a zaben shugabancin kasar mai zuwa na 2018.