Likitoci A Asbitocin Gwamnatin Sun Bada Sanarwan Shiga Yajin Aiki A Nigeria
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i23687-likitoci_a_asbitocin_gwamnatin_sun_bada_sanarwan_shiga_yajin_aiki_a_nigeria
Kungiyar likitoci masu koyon karatu sun bada sanarwan fara yajin aiki na gama gari a duk fadin kasar don neman wasu hakkokinsu wadanda suka makali a hannun gwamnatocin tarayyar da kuma na jihohi a ranar 4 ga watan satumba mai kamawa.
(last modified 2018-08-22T07:00:37+00:00 )
Aug 31, 2017 01:56 UTC
  • Likitoci A Asbitocin Gwamnatin Sun Bada Sanarwan Shiga Yajin Aiki A Nigeria

Kungiyar likitoci masu koyon karatu sun bada sanarwan fara yajin aiki na gama gari a duk fadin kasar don neman wasu hakkokinsu wadanda suka makali a hannun gwamnatocin tarayyar da kuma na jihohi a ranar 4 ga watan satumba mai kamawa.

Jaridar Primium times ta Nigeria ta nakalto shugaban kungiyar  likitocin wacce aka fi sani da NARDs  a takaice  Dr Olushegun Olaopa na jami'ar koyon aikin likita ta Ibadan yana bada wannan sanarwan a jiya Laraba. Ya kuma kara da cewa a ranar Litinin dukkan yayan kungiyar zasu dakatar da aiki don takurawa gwamnatoci kan albashinsu da kuma wasu bukatunsu da suka makale a wajensu.

Olushegunn ya ce a ranar 26 ga watan Augustan da muke ciki ne shuwagabannin kungiyar suka gudanar da tare a Abuja don tattauna matsalolin kungiyar da kuma matakan da zasu dauka don warwaresu. shi ne a karshen taron suka tsaida ranar 4 ga watan Satumba don fara yajin aiki na sai baba ta gani, sai har an bayasu hakkokinsu.

Shugaban kungiyar ta NARDs ya kammala da cewa zasu gudanar da yajin aikin gargadi a ranar 30  ga watan Augusta a dukkan rassansu dake dukkan jihohin kasar .