Harin Ta'addanci Ya Lashe Rayukan Mutane A Kasar Somaliya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i23911-harin_ta'addanci_ya_lashe_rayukan_mutane_a_kasar_somaliya
Wani bom ya fashe a gidan cin abinci da ke garin Beledweyne a shiyar arewacin kasar Somaliya, inda ya lashe rayukan mutane akalla shida tare da jikkata wasu da dama.
(last modified 2018-08-22T07:00:40+00:00 )
Sep 10, 2017 13:41 UTC
  • Harin Ta'addanci Ya Lashe Rayukan Mutane A Kasar Somaliya

Wani bom ya fashe a gidan cin abinci da ke garin Beledweyne a shiyar arewacin kasar Somaliya, inda ya lashe rayukan mutane akalla shida tare da jikkata wasu da dama.

Majiyar rundunar 'yan sandan kasar Somaliya ta sanar da cewa: Wani bom ya tarwatse a gidan cin abinci a garin Beledweyne da ke arewacin kasar Somaliya, inda fashewarsa ya janyo hasarar rayukan mutane akalla shida tare da jikkatan wasu adadi masu yawa.

Majiyar 'yan sandan ta kara da cewa: Gidan cin abincin yana kusa ne da gidan wani babban jami'in gwamnatin kasar,  kuma tuni kungiyar ta'addanci ta Al-Shabab ta kasar ta dauki alhakin kai harin.